FALALAR DAKE CIKIN WATAN RAMADAN

 


Watan Ramadan yanada falala mai yawa kuma masu tarin albarka, kadan daga cikinsu sune:

1.Allah subhanahu wata'ala ya saukarwa manzon Allah s.a.w littafin dayafi komai girma aduniya wato alqur'ani .

2.Allah s.w.a yana ninkawa bayinsa lada akan dukkan wata ibada dasukayi ko meye qaramcinta misali idan kayi salati 1 Allah zai saka mala'ikunsa suyima 10 amma kuma watan Ramadan Allah zai saka mala'ikunsa suyima 20 sakamakon falalar watan Ramadan.




3. Allah s.w.a yana saukarwa bayinsa da abubuwa guda 3 acikin watan Ramadan wayannan abubuwan sune Rahama,Gafara,Tsira.


4.Allah s.w.a yabamu dare Wanda yake dauke da cikakkiyar falala wadda take ibada cikin wannan Daren tafi ibadar wata dubu    ( shekara 83 da kwana 22 ) ayayinda wannan Daren yanazuwane cikin darerai 10 na karshen watan Ramadan .


Dan haka yan'uwana mezai Hana mudage akan neman wannan falalar mukasance masu ambaton Allah akowane lokaci  domin neman dacewa da rahamar Allah da jinkansa.



Ya Allah muna roqonka kabamu albarkar dake cikin wannan wata mai albarkar.