Ko kun san dan Najeriyar da ke sauya akalar kwallon kafa a Saudiya?

Sabon daraktan a gasar kwararru ta Saudi Arabiya, Michael Emenalo ya karbi ragamar sauya fuskar kwallon kafar kasar.

Emenalo na jagorancin cibiyar siyan ƙwararrun ƴan wasa don samar da tsari mai mahimmanci don jawo hankalin ƙarin 'yan wasan duniya masu daraja.

Hukumar kwallon kafar kasar ta ce tsohon daraktan na Chelsea zai taimaka ta hanyar inganta darajar 'yan wasan da ke gasar.

Hukumar ta ce ta nada Emenalo, wanda ya kula da daukar 'yan wasa a Chelsea tare da sake fasalin makarantar horar da 'yan kwallon kungiyar a lokacin da yake daraktanta daga 2011 zuwa 2017,ya "tabbatar da makoma 'yan wasa mai inganci''.